• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Harin ‘Yan Daba: NAWOJ Ta Jajantawa Ma’aikatan Pyramid FM Kano

Khadija Maitaya by Khadija Maitaya
September 11, 2026
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

NAWOJ Ta Jajantawa Ma’aikatan Pyramid FM Kano Kan Harin ‘Yan Daba
Ƙungiyar Mata ‘Yan Jarida ta Ƙasa, NAWOJ, reshen Jihar Kano, ta kai ziyarar jajantawa ga shugabannin gidan Rediyon Najeriya Pyramid FM Kano, bisa harin da wasu da ake zargin ‘yan daba ne suka kai wa wasu daga cikin ma’aikatan gidan rediyon, tare da farfasa gilasan motar gidan jim kaɗan bayan kammala taron jam’iyyar APC a jihar.

Shugabar ƙungiyar NAWOJ reshen Jihar Kano, Hajiya Bahijja Malam Kabara, ta ce sun kai ziyarar ne domin jajantawa ma’aikatan gidan rediyon tare da bayyana rashin jin daɗinsu bisa wannan mummunan lamari.

RelatedPosts

Gwamna Abba Kabir Ya Dauki Babban mataki na kawar Da Matsalar Tsaro A Jihar Kano

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Hajiya Bahijja Kabara ta ce ba za a lamunci wasu bata-gari su riƙa kai wa ‘yan jarida hari ba, musamman a lokacin da suke gudanar da aikinsu ko kuma kan hanyarsu ta dawowa daga wuraren ɗaukar rahotanni.

Ta buƙaci gwamnati da hukumomin tsaro da su ɗauki matakin da ya dace, tare da gudanar da bincike domin gano waɗanda suka aikata wannan aika-aika da kuma hukunta su bisa doka.

Shugabar NAWOJ ta kuma yi kira ga shugabannin siyasa da su ja kunnen magoya bayansu, tare da tabbatar da cewa ba su kai wa ‘yan jarida hari ba yayin da suke gudanar da aikin ɗaukar rahotannin tarukan siyasa da gangamin yaƙin neman zaɓe, musamman a yayin da ake tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.

Kazalika, Hajiya Kabara ta buƙaci hukumomin tsaro a Jihar Kano da su gudanar da cikakken bincike kan lamarin, tare da hukunta duk wanda aka samu da hannu, domin hakan ya zama darasi ga sauran masu irin wannan ɗabi’a.

Da yake mayar da jawabi, Mukaddashin Shugaban Gidan Rediyon Najeriya Pyramid FM Kano, Malam Umar Nuhu, ya bayyana farin cikinsa, a madadin sauran shugabannin gidan rediyon, bisa ziyarar jajantawar da shugabannin NAWOJ suka kawo musu a matsayin abokan aiki.

Malam Umar Nuhu ya ce suna matuƙar godiya ga ƙungiyar, yana mai cewa irin wannan lamari ba zai karya musu gwiwa ba, illa ma zai ƙara musu ƙwarin gwiwa wajen ci gaba da gudanar da aikin ɗaukar rahotannin harkokin siyasa da sauran ayyukan jama’a.

Ya ce ma’aikatan gidan rediyon za su ci gaba da gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa, gaskiya da adalci, musamman yayin da ƙasar ke tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Gwamna Abba Kabir Ya Dauki Babban mataki na kawar Da Matsalar Tsaro A Jihar Kano

Khadija Maitaya

Khadija Maitaya

RelatedPosts

Gwamna Abba Kabir Ya Dauki Babban mataki na kawar Da Matsalar Tsaro A Jihar Kano
LABARAI

Gwamna Abba Kabir Ya Dauki Babban mataki na kawar Da Matsalar Tsaro A Jihar Kano

by Abdulhamid Isa
September 7, 2026
Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Abin Mamaki, Karon farko Najeriya ta ƙera jirgin yaƙi Maras Matuƙi

Abin Mamaki, Karon farko Najeriya ta ƙera jirgin yaƙi Maras Matuƙi

January 24, 2026
Sabon CP na Jihar Sokoto Ya Nemi Goyon Bayan Sarkin Musulmi

Sabon CP na Jihar Sokoto Ya Nemi Goyon Bayan Sarkin Musulmi

June 4, 2026
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Gwamna Abba Kabir Ya Dauki Babban mataki na kawar Da Matsalar Tsaro A Jihar Kano

Gwamna Abba Kabir Ya Dauki Babban mataki na kawar Da Matsalar Tsaro A Jihar Kano

September 7, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026
Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

August 23, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media