Tun da fari, kafar yaɗa labaran ta wallafa rahoto da ke nuna cewa gwamnatin Jihar Kano ce ke da hannu wajen raba kayan, lamarin da ya haddasa suka da martani daga jama’a musamman a kafafen sada zumunta.
Sai dai daga bisani, ƙungiyar Kano Development Forum ta shiga lamarin inda ta aikewa kamfanin wasiƙa, tana neman a goge labarin tare da yin cikakken bayani domin gyara abin da ta bayyana a matsayin rahoto mai ruɗarwa.
Bayan wannan matsin lamba, Pulse Nigeria ta cire labarin daga shafinta tare da wallafa sabon bayani, inda ta amince cewa an fitar da rahoton ba tare da cikakken bincike ba, kuma bai bayyana ainihin yadda lamarin ya faru ba.
Kamfanin ya kuma bayyana cewa bai fayyace tun farko cewa gwamnatin Kano ba ce ke da alhakin abin da ya faru ba, yana mai cewa hotunan da suka yadu sun fi alaƙa da magoya bayan siyasa ne, ba wani shiri na gwamnati ba.
A cikin sanarwar neman afuwar, Pulse Nigeria ta ce yadda aka rubuta labarin ya haifar da ruɗani tare da illa ga martabar al’ummar Kano da gwamnatin jihar.
A nata ɓangaren, ƙungiyar Kano Development Forum ta yaba da gyaran rahoton, tana mai cewa hakan alama ce ta ɗaukar alhaki a aikin jarida. Ta kuma jaddada cewa gaggawar wallafa labarai ba tare da tantance gaskiya ba na iya lalata amincin kafafen yaɗa labarai.
Rahotanni sun nuna cewa ce-ce-ku-cen ya samo asali ne daga wasu hotuna da aka ɗauka yayin wani taron siyasa na jam’iyyar APC domin tarbar uwargidan shugaban ƙasa, Oluremi Tinubu, a Kano.
Wasu mazauna jihar sun bayyana cewa lamarin ya fi nasaba da alamu na siyasa da ayyukan magoya baya, ba wani tsari na gwamnatin jihar ba.










