Hukumar Gudanarwa ta makarantar shahada Islamiyaya dake unguwar yalwa Gwauran dutse karamar hukumar Dala, ta shawarci dalibai da su kasance masu amfani da ilimin da suka samu ta hanyoyin da suka dace,domin tsira a gobe Alkiyama.
Shugaban makarantar malam umar yahaya ne ya ba da shawarar a lokacin da yake zantawa da manema labarai Jim-kadan bayan kammala saukar karatun Al,kur’ani maigirma wanda daliban makarantar suka yi a harabar makarantar dake unguwar yalwa anan birnin kano
. mal.umar yahaya yace amfani ilimi a gurin Dan Adam shine ,ya rika amfani dashi domin bautawa Allah subahanahu wata,ala da aiwatar da shi a cikin Rayuwarsa ta yau da kullum,inda yace,ilimi yana daya daga cikin abubuwan dake setawa Al,umma Rayuwarsu.
Shima anasa jawabin 6 malam yahaya Bala daya daga cikin malaman wannan makaranta yayikira ga masu Ruwa da tsaki da mahukunta da masu hannu da shuni dasu kasance masu taimakawa irin Wadan nan makarantu domin ciyar da harkokin ilimi gaba kasancewa ilimi shine kan gaba wajen ingata Rayuwar A












