DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Dubun malaman jami’ar na bogin ta cika ne a yayin da suke tsaka da sayar wa dalibai ’yan ajin farko da litattafan karatu.
Sanarwar da jami’ar ta fitar ɗauke da sa hannun Mukaddashin Magatakarda Jami’ar BUK Bala G. Abdullahi, ta ce lakcarorin bogin sun tursasa dalibai sayen litattafansu guda hudu a matsayin sharadin cin jarabawar darussan su.
Ya ce dubun mutanen biyu, Mista David Iluebe daga Jihar Edo da Mista Chike E. Eke daga Jihar Delta, ta cika ne bayan sun shiga dakin karatu a Tsangayar Karatun Injiniya, suka gabatar da kansu a matsayin lakcarori, suka tallata musu litattafai hudu.
Lakcarorin ba su tsaya nan ba, sun bayyana wa daliban cewa sayen litattafan wajibi ne kuma babu wanda zai ci jarabawa sai wanda ya saya.












