• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

CBN ya musanta cewa ba shi da isassun takardun buga sabon kuɗi

aksam by aksam
February 11, 2023
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Babban Bankin Najeriya CBN ya musanta rahotonnin da ke cewa gwamnan bankin Godwin Emefiele ya alaƙanta rashin wadatattun takardun buga sababbin kuɗi a ƙasar, kan ƙarancin takardun buga kuɗin.

Jaridar PREMIUM TIMES a ƙasar ce dai ta ruwaito wata majiya na shaida mata cewa Godwin Emefiele ya bayyana wa taron majalisar magabatan ƙasar cewa rashin isassun takardun buga kuɗi ne ya haddasa ƙarancin takardun sababbin kuɗin a ƙasar.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

To amma a wata sanarwa da CBN ɗin ya fitar ya ce babu inda gwamnan banki ya faɗi haka a lokacin da yake yi wa majalisar magabatan jawabi ranar Juma’a a fadar shugaban ƙasar.

Sanarwar ta ƙara da cewa abin da Mista Emefiele ya faɗa wa majalisar shi ne hukumar da ke lura da buga kuɗin na aikin buga kuɗin domin wadata ‘yan ƙasar da takardun kuɗin da suke buƙata domin harkokinsu na yau-da-kullum.

”Hukumar da ke Lura da Buga Kuɗi ta Ƙasa tana da isassun kayan aikin da take buƙata wajen buga sabbin kuɗin da za su wadatar. Dan haka CBN ke kira ga jama’a da su yi watsi da rahotonnin da ke cewa babu isassun takardun buga kuɗin tare da kiran jama’a su ƙara haƙuri, kasancewar muna bakin ƙoƙarinmu wajen ganin mun ƙara yawan kuɗin da ke yawo a hannun mutane”, in ji sanarwar.

Haka kuma sanarwar ta ce akwai wani sautin murya da ke yawo a shafukan sada zumunta wanda ke zargin cewa CBN na shirin rufe wasu bankuna a ƙasar, musamman a wasu yankunan ƙasar.

Dan haka sanarwar ta ce CBN ba shi da wannan shiri, kuma saƙon da ke cikin muryar ya saɓa wa dokar tsarin banki na ƙasar.

Dan haka CBN ɗin ya shawarci ‘yan ƙasar da su yi watsi da saƙon sautin muryar kasancewar ba daga bankin yake ba.

Tags: CBNGodwin Emefiele
Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Next Post

Kotun Ƙolin Najeriya ta gargaɗi masu sukar hukuncinta kan Ahmad Lawan da Akpabio

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Karin harajin VAT, Atiku ya yi kakkausar suka ga Tinubu karanta abin da ya fada

Karin harajin VAT, Atiku ya yi kakkausar suka ga Tinubu karanta abin da ya fada

September 8, 2024
Gamaiyar kungiyar NLC da TUC sun sanar da lokacin tsunduma yajin aikin sai baba ta gani

Gamaiyar kungiyar NLC da TUC sun sanar da lokacin tsunduma yajin aikin sai baba ta gani

May 31, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media