• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Kano ‘Ba Za Ta Yi Katsalandan A Shari’ar Da Ake Yi Wa Murja Kunya Ba

aksam by aksam
February 19, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home KOTU
ADVERTISEMENT
468
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA

“Sai dai an shaida wa gwamnati cewa an sake samun wani sabon zargin da ake yi mata wanda ya sa jami’an tsaro suka fitar da ita daga gidan gyaran halin domin bincike” a cewar sanarwar mai ɗauke da sa hannun Kwamishina Watsa Labarai, Baba Halilu Dantiye a ranar Litinin.

RelatedPosts

Yanzu-Yanzu: Kotun Koli Ta Tabbatar Da Sanata David Mark a Matsayin Halastaccen Shugaban Jam’iyyar (ADC) Na Kasa

Kotun Koli ta yanke hukuncin kan rikicin jam’iyyar PDP

Kotu Ta Yanke Wa Umar Idris Farawa Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Bisa Samun sa Da Laifi

Ta kuma ce har yanzu shari’arta ba ta mutu ba, kuma za ta ci gaba har zuwa matakin ƙarshe da kotu za ta yanke hukunci,

Gwamnatin ta ce ta fitar da sanarwar ce saboda “An jawo hankalin gwamnatin Jihar Kano kan wani zargi mara tushe da ake yaɗawa a shafukan sada zumunta kan cewa da hannunta a sakin Murja Ibrahim Kunya da aka yi daga gidan yari, wacce take fuskantar shari’a a kan watsa bidiyon da suka take wasu dokokin jihar.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “waɗannan zarge-zarge kwata-kwata ba su da tushe balle makama, ba gaskiya ba ne, wani hasashe ne marar tushe na wasu ɓata-gari da suke so su baƙanta gwamnati da Gwamnan Jihar Alhaji Abba Kabir Yusuf a idon al’umma.

A makon da ya gabata ne Hukumar Hisbah a Kano ta kama Murja Ibrahim Kunya inda har ta gurfanar da ita a gaban kotu bisa wasu zarge-zarge da suka haɗa da yin bidiyon rashin tarbiyya a kafafen sada zumunta.

Kotun ta tura ta gidan gyaran hali da niyyar zuwa ranar da za a koma sauraron shari’ar, amma daga baya hukumar gidan yarin ta sake ta bayan da ta ce ta samu takardar daga kotu.

Gwamnatin jihar ta ce tana sane da tanadin da kundin tsarin mulkin kasar ya yi na raba madafun iko da ma’auni tsakanin bangaren shari’a da na majalisa da na zartarwa a matsayin bangarori uku na gwamnati, kuma ba za ta taɓa yin wani abu da zai kawo cikas ga wannan tsari ba.

Gwamnati tana sane da cewa batun na doka ne da yake cikin tsarin shari’a kuma ba za ta taɓa yin katsalandan ta kowace hanya don yin tasiri wajen samar da adalci ba.

Sanarwar gwamnatin ta kuma tunatar da al’umma cewa abin da ta sani a kan batun shi ne cewa an gurfanar da Murja Kunya a gaban wata Kotun Shari’a da ke Kwana Hudu a karamar hukumar Nassarawa bisa zargin ta da yada wasu munanan bidiyoyi a dandalin sada zumunta, inda kotu ta bayar da umarnin hakan tare ta a gidan gyaran hali kafin a ci gaba da sauraron shari’ar a ranar Talata, 20 ga Fabrairun 2024 bayan ta saurari bukatar neman belinta.

A ƙarshe gwamnatin ta yi kira ga jama’a da su yi watsi da zargin da ake yi mata, tana cewa ba wani abu ba ne illa ƙoƙarin ɓata mata suna tare da tabbatar wa al’ummar jihar cewa za ta ci gaba da mutuntawa tare da kiyaye alfarmar tanadin kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya.

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

BREAKING: Tinubu returns to Abuja after AU Summit in Addis Ababa

Next Post

Kotu ta yanke wa Ramlat prince hukunci Kala uku wasu da zabin tara

aksam

aksam

RelatedPosts

Yanzu-Yanzu: Kotun Koli Ta Tabbatar Da Sanata David Mark a Matsayin Halastaccen Shugaban Jam’iyyar  (ADC) Na Kasa
KOTU

Yanzu-Yanzu: Kotun Koli Ta Tabbatar Da Sanata David Mark a Matsayin Halastaccen Shugaban Jam’iyyar (ADC) Na Kasa

by aksam
April 30, 2026
Yau Ake Sa Ran Kotun Koli Ta Najeriya Zata Yanke Hukunci A Yau Kan Rikicin Shugabancin  Jam’iyyar ADC A Matakin Kasa
KOTU

Kotun Koli ta yanke hukuncin kan rikicin jam’iyyar PDP

by aksam
April 30, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Umar Idris Farawa Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Bisa Samun sa Da Laifi
KOTU

Kotu Ta Yanke Wa Umar Idris Farawa Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Bisa Samun sa Da Laifi

by aksam
April 22, 2026
Yau Ake Sa Ran Kotun Koli Ta Najeriya Zata Yanke Hukunci A Yau Kan Rikicin Shugabancin  Jam’iyyar ADC A Matakin Kasa
KOTU

Yau Ake Sa Ran Kotun Koli Ta Najeriya Zata Yanke Hukunci A Yau Kan Rikicin Shugabancin Jam’iyyar ADC A Matakin Kasa

by aksam
April 22, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Kungiyar yantebura ta IBB jikin masallacin Idi ta yi cikakken jawabi a kan abin da ya faru a baya.

Kungiyar yantebura ta IBB jikin masallacin Idi ta yi cikakken jawabi a kan abin da ya faru a baya.

June 17, 2024
Ƙasashen Turai sun fara maye gurbin manyan kamfanonin fasaha na Amurka da na cikin gida

Ƙasashen Turai sun fara maye gurbin manyan kamfanonin fasaha na Amurka da na cikin gida

January 25, 2026
ADVERTISEMENT

Trending.

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media