Wani bam da ya tashi ya kashe Almajirai huɗu da manyan mutane mutum biyu a ƙaramar hukumar Gubio dake jihar Borno.
Jaridar Daily Trust ta ce da yake tabbatar da faruwar lamarin, shugaban ƙaramar hukumar Gubio, Alhaji Mali Gubio, ya ce lamarin ya faru ne a wani ginin da ba a kammala ba da misalin ƙarfe 11:00 na safe, a ranar Asabar.
Duk mutanen da abin ya shafa sun mutu don haka ba za mu iya sanin ainihin abin da ya faru ba, amma fashewar bam ne a wani gida da aka ajiye ƙarafa.
“An gano gawarwakin Almajirai huɗu da manya mutane mutum biyu, amma ba mu iya tantance gawarwakin manyan mutanen biyu ba da aka gano gawarsu a wurin ba, kuma babu wanda ya zo ɗaukarsu.
” Ya ce gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum, ya hana jari-bola a jihar domin hana ɓarnatar da kayayyakin gwamnati a yankunan da ba kowa.
Ya ce mutane da yawa sun yi imanin cewa, ba da saninsu ba ne masu jari-bolan suka tattara tare da adana bam ɗin tare da wasu ƙarafa a ginin da ke kusa da makarantar Alqur’anin
(Tsangaya), cewar rahoton jaridar Vanguard.












