Hukumar Gudanarwar makarantar MADARASATUL AHBABUL MUSDAFA (S A W) Islamiyaya dake unguwar gobirawa bayan makarantar madaki A karamar hukumar Dala,ta shawarci dalibai da su kasance masu amfani da ilimin da suka samu ta hanyoyin da suka dace,domin tsira a gobe Alkiyama.
Shugaban makarantar malam Sunusi Abubakar ne ya ba da shawarar a lokacin da yake zantawa da manema labarai Jim-kadan bayan kammala saukar karatun Al,kur’ani maigirma wanda daliban makarantar suka yi A Dakin taro nasa,adu zungur dake gwammaja anan birnin kano .
mal.Sunusi Abubakar yace amfani ilimi a gurin Dan Adam shine ,ya rika amfani dashi domin bautawa Allah subahanahu wata,ala da aiwatar da shi a cikin Rayuwarsa ta yau da kullum,inda yace,ilimi yana daya daga cikin abubuwan dake setawa Al,ummaRayuwarsu.
Shima anasa bangaran Dagacin gobirawa mal. Musa Isa muhammad yayikira ga masu Ruwa da tsaki da mahukunta da masu hannu da shuni dasu kasance masu taimakawa irin Wadan nan makarantu domin ciyar da harkokin ilimi gaba kasancewa ilimi shine kan gaba wajen ingata RayuwarAl,umma .
Hakazalika shima anasa bangaren Labaran Sani Adakawa chanchanta.Wakilin Danmajalistar taraiya nakaramar hukumar Dala. Aliyu sani madaki yayabawa malaman kan irin kokarin dasuke naganin sundora al,umma akan hanyar data dace yakara dacewa kofarsu abude take domin tallafawa harkokin Adinin musulinci takowace fuska
Haka zalika suma anasu bangaran daliban sukemanin guda (40) indasuka godewa
Allah subahanahu wata,ala dayanunamusu wanan rana maimutukar tarihi arayuwar su .sunkuma godewa malamansu da kuma iyayensu wajan daukar nauyi da dawainiyar su yayin Neman karatu.
Daliban sun sha Al,washin yin Amfani da ilimin da suka samu wajan yin biyayya ga Allah subahanahu wata,ala da taimakawa sauran Dalibai yanbaya.
Ayayin taron saukardai ankadamar dawani sabon litafi maidauke da bayanai daban daban dasuka kinshi zamantakewa tarayuwa musamman abangaran daya shafi aure.
angudanar danasihohi da dama dagabakin manyamanyan malamai daban daban .











