Mai alfarma sarkin Musulmi ya nuna damuwarsa kan yadda kullum ‘yan ta’adda ke yin wasa da hankalin jami’an tsaro wajen kai hare-hare
Alhaji Sa’ad Abubakar III ya ce jami’an tsaro da gwamnati ba sa iya samun bayanan sirri har sai ‘yan bindiga sun gama cin karensu ba babbaka
Sarkin ya bayyana hakan ne a jihar Bauchi, yayin da ya ke martani kan kisan gillar da ‘yan ta’adda suka yi wa mutane a jihar Filato
Ya yi kira ga jami’an tsaro da su zamo masu kara kaimi wajen ayyukan leken asiri a kasar don samun bayanan sirri da zasu rinka dakile hare-haren ‘yan bindiga,
Alhaji Abubakar III ya ce: “Kullum ba mu da aiki sai yin Allah wadai, kuma ihu ne bayan hari, daga nan me muke tsinanawa?
Da farko Tudun Biri, yanzu kuma Filato, shin ina gwamnati mai kare al’umma?”
“Me ya sa jami’an tsaro ba za su rinka samun bayanan sirri don kare faruwar hare-haren ba?
Me ya samu fannin fikirar jami’an kasar nan?
Kuna nufin ba wanda ke da masaniya kan hare-haren nan?”










