• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yau Shekaru 12 Da Rasuwar Sarkin Kano, Marigayi Ado Bayero

aksam by aksam
June 6, 2026
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga: Hassan Umar Gwammaja

Alhaji Dr. Ado Abdullahi Bayero (1930–2014), Sarkin Kano na 13 kuma mafi dadewa a tarihin masarautar Kano, ya kasance ɗaya daga cikin manyan sarakunan gargajiya da suka yi tasiri a Najeriya da nahiyar Afirka baki ɗaya.

RelatedPosts

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

A ranar 22 ga Oktoban 1963 ne ya hau karagar mulkin Kano yana da shekaru 33 a duniya, inda ya yi mulki sama da shekaru 50 har zuwa rasuwarsa a ranar 6 ga Yunin 2014.

An haifi Sarkin ne a gidan sarautar Fulani Sullubawa, kasancewarsa ɗan marigayi Sarkin Kano, Alhaji Abdullahi Bayero. Kafin hawansa karagar mulki, ya yi ayyuka daban-daban da suka haɗa da ma’aikacin banki a ‘Bank of British West Africa’, ɗan majalisar yankin Arewacin Najeriya, Wakilin Doka na hukumar mulkin gargajiya ta Kano da kuma jakadan Najeriya a ƙasar Senegal.

Marigayi Ado Bayero ya yi fice wajen haɗa kan al’umma, inda ya kasance abin koyi wajen zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabambantan kabilu da addinai. A lokacin Yaƙin Basasar Najeriya, an yaba masa kan rawar da ya taka wajen kare rayuka da dukiyoyin ’yan kabilar Igbo da suka nemi mafaka a Kano.

A bangaren al’adu kuwa, ya taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa bikin hawan sallah na Kano, wanda ya zama ɗaya daga cikin manyan abubuwan yawon buɗe ido da al’adun gargajiya a Arewacin Najeriya.

Haka kuma ya kasance jagora a harkokin addinin musulunci, mai goyon bayan ilimin addini da na zamani, tare da kasancewa ɗaya daga cikin manyan jagororin darikar Tijjaniyya a Najeriya.

Duk da ƙalubalen tsaro da ya fuskanta, ciki har da harin da aka taba ayarinsa a shekarar 2013, marigayi sarkin ya ci gaba da jagoranci cikin jajircewa. Harin ya yi sanadin mutuwar direbansa da mai tsaronsa, yayin da wasu daga cikin ’ya’yansa suka samu raunuka.

A ranar 6 ga Yunin 2014 ne Allah Ya yi wa sarkin rasuwa a fadarsa ta Gidan Rumfa yana da shekaru 83. Jana’izarsa ta samu halartar dubban jama’a da manyan baki daga sassa daban-daban na Najeriya da ƙasashen waje.

Marigayi Ado Bayero ya bar manyan ’ya’ya da suka taka muhimmiyar rawa a harkokin mulkin gargajiya dama gwamnati, ciki har da Alhaji Sanusi Ado Bayero, Alhaji Aminu Ado Bayero wanda daga baya ya zama Sarkin Kano na 15, da kuma Alhaji Nasiru Ado Bayero wanda ya taba zama sarkin Bichi.

A yau shekaru bayan rasuwarsa, ana ci gaba da tuna Marigayi sarkin Kano Ado Bayero a matsayin ɗaya daga cikin fitattun sarakunan gargajiya da suka yi tasiri wajen zaman lafiya, ci gaban ilimi, bunƙasa al’adu da haɗin kan Najeriya.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Next Post

Rasha Na Kara Amfani da Aljeriya a Matsayin Cibiyar Ayyukan Sojinta a Afirka

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026
Badakalar shugabanni a Amurka Ta Tayar da Muhawara A Matsayin Ta Na Jagorar Duniya
LABARAI

Badakalar shugabanni a Amurka Ta Tayar da Muhawara A Matsayin Ta Na Jagorar Duniya

by Khadija Maitaya
June 10, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Ta tabbata Tinibu ba shi ya ci zabe ba Karanta kalaman shugaban INEC

Ta tabbata Tinibu ba shi ya ci zabe ba Karanta kalaman shugaban INEC

March 6, 2024

Top Strategies for Winning at Casino War at casigood casino

April 21, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media