Kungiyar Masu hada hadar kudaden canji ta Kasa reshen jihar Kano, ta bayyana jin dadinta bisa kara raguwa da farashin kudaden waje suka yi a Kasuwannin ‘Yancanji dake fadin kasar nan.
Shugaban Kungiyar Alh.Sani Dada ne ya bayyana haka a lokacin da yake Zantawa da Manema labarai a ofishinsa dake kasuwar canji ta Wapa dake nan Kano.
Sani Dada yace,rage farashin kudaden waje da Babban Bankin Kasa yayi, zai fitar da Masu hada hadar canji daga zarge zargen Alumma na cewa sune suke da alhakin tashin gwauran zabi da kayayyakin Masarufi Suka yi a Kasuwannin Kasar nan.
Shugaban yace,wannan Kalubale na tsadar kayayyakin Masarufi ta rage tsakanin yankasuwa da Alummar Kasar nan, saboda yanzu jama’a za su fahinci inda gizo yake saka.
Sani Dada yace, Kungiyar masu hada hadar canji ta Wapa ta himmatu wajen ganin an kara inganta rayuwar matasa musamman, ‘Ya’yan Kungiyar masu hada hadar canji domin rage marasa ayyukan yi da kuma, farfado da tattalin Arzikin Najeriya.
Daga karshe Shugaban ya bayyana cewa, Kungiyarsa a shirye take wajen baiwa Gwamnati cikakken hadin kai domin ciyar da jihar Kano da ma Kasa baki daya.
Ibrahim sani gama pyramid.












