Dakatar da Minista Betta Edu da Shugaban kasa Tinubu ya yi a kan badakalar kudi naira miliyan 585 ya haddasa cece-kuce a soshiyal midiya
Da yake tsokaci, Sanata Shehu Sani, ya bayyana cewa binciken EFCC ya aike da sako karara kan mahimmancin bin diddigi a gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Tinubu
Tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya ya yi furucin ne a dandalin sada zumunta na X wanda aka fi sani da Twitter a da in furucin ya haddasa cece-kuce a tsakanin jama’a game da bambancin tsarin shugabancin Tinubu da na Buhari











