Bayan shafe shekaru uku ana aikin ginin gadar Sama dake tal’udu a yankin karamar Hukumar birni an samu gagarumin ci gaba a aikin gadar.
Jami’ar hulda da jamaa ta Ma’aikatar Ayyuka Hajiya saudatu Muktar Adnan ce ta bayyana hakan a tattaunawar ta da wakiliyarmu kadija maitaya.
Ta bayyana cewa ana ci gaba da aikin ba dare ba rana domin samun nasarar kammala aikin bisa tsarin da aka tsara.
Ta bayyana cewar aikin ya samar da guraben ayyukan yi ga mazauna yankin, yayin da aka yi wa wasu sassan hanya kwalta, tare da gyaran magudanan ruwa domin rage ambaliya.
Haka kuma, an faɗaɗa wasu sassan hanya domin rage cunkoson ababen hawa da inganta zirga-zirga.
Ana sa ran cewa kammala gadar zai inganta sufuri tare da bunƙasa harkokin kasuwanci a yankin.
A nasu ɓangaren, ‘yan kasuwa da ke kusa da wurin aikin sun nuna gamsuwa da yadda aikin ke tafiya, suna masu cewa kammalashi zai kawo sauƙi ga harkokinsu na yau da kullum.
Sun yabawa gwamnain jihar Kano bisa kokarinta na Samar da abababen more rayuwa ga al umar jihar Nan











