A yanzu haka tsohuwar ministar harkokin jin kai, Sadiya Umar-Farouq, ta mika kanta domin bincike a hedikwatar hukumar EFCC da ke Abuja.
Tsohuwar ministar, wadda ake tuhumar ta da karkatar da kudi har naira biliyan 37.1 ta hannun wani dan kwangila, James Okwete, ta isa ofishin EFCC ne a safiyar ranar Litinin.
A bisa ga ra’ayi na, na isa hedikwatar hukumar EFCC domin karrama goron gayyata da hukumar ta yi mun na bayar da karin haske kan wasu batutuwan da hukumar ke bincike a kansu.”
I have, at my behest, arrived at the headquarters of the Economic and Financial Crimes Commission (EFCC) to honour the invitation by the anti-graft agency to offer clarifications in respect of some issues that the commission is investigating.
— Sadiya Umar Farouq CON (@Sadiya_farouq) January 8, 2024












